Posts

Showing posts from March, 2024

IYAMMU

Image
IYAMMU Hajiƴa Iyammu wata tsohuwa ce wadda ke da kyakkyawar zuciyar rainon yara mata marayu kuma tsayawa akan karatun su da tarbiyyar su. Ta raini yara masu tarin yawa kuma har zuwa kayan ɗaki da gara ta ke yi musu idan an ta shi aurar da su. Saboda shekarunta ne kowa ya ke kiranta Hajiya Iyammu. Ta kan shiga lamarin duk wasu waɗanda ta fuskanci suna cikin buƙata a gidajen maƙobta da ma waɗanda ta samu labarin su waɗanda ke nesa da ita. Allah mai ikonsa duk gwagwarmayar rayuwa da aure auren da ta yi Allah bai nufa zata samu ɗa ba ballantana ma jika a rayuwarta. Wannan ya sanya ta cigaba da ayyukan alheri da duk dukiyar da ta mallaka domin kuwa idan ta bar su ma ba ta wani tartibin magaji sai dai a dangin dangiro na can nesa. Tun lokacin da ta ke da jininta a jika ta ke harkar safara zuwa ƙasashen Kurmi. A can ne ta ke saro murjani da sauran duwatsun da ake samowa daga teku ta kawo su nan Arewa domin sayarwa ga ƴan kasuwar shinku da ke neman su ruwa a jallo saboda manyan sarakuma da att...

MALAM MAI DARA

Image
MLAAM.MAI DARA Wata rana wani maharbi ya shiga jeji da bakar sa rataye a kafaɗa domin farauta. Ya sanya bunjuma taɓfarin saƙi da jar dara akan sa sanann kuma ya na goye da kibau a bayan sa. Bayan ya gama zagaya daji bai samu wani abinda zai iƴa farautowa ba sai ya hangi wata ƴar ƙaramar tsuntsuwa a kan bishiya. Sai ya ce a ra sa " Bari na harbo tsuntsuwar nan ko.ɗan gasawa nayi na ci da dare." Bayan ya gama auna ƴar tsuntsuwa zai harba sai ya ji ta na yin wata waƙa ta na cewa: Aauna ni a hankali Malam mai Dara Kar ka je ka yi rauni Malam mai Dara" Sai da ya gama auna ta sarai sai dai ya sake jin ta na cewa: "Hahharbo ni a hankali Malam mai dara Kar kaje ka yi rauni Malam mai Dara" Yayimda ya ƙara kasa kunne sosai sai dai ya ji cewa tabbas da shi wannan ƴar tsuntsuwar nan ta ke yin wannan waƙar tata ba wai jin kunne ya yi ba. Har ya yi kamar ya fasa harbinta ya dawo gida abin sa, sai wata zuciyar kuma ta ce masa "Kai wane irin hatsabibin kwaro ne ma baka ta...

AUTA DA DODO

Image
AUTA DA DODO Auta yaro ne jarumi mai son yawace-yawace zuwa ƙashashe daban daban domin nuna bajiɓta da kuma jarumtar sa. Ya baro gida Maraɗi tun yana da shekaru goma inda ya ke ta wuce manya ƙasashe da garuwa bayan ya nuna wata bajinta ta gani ta faɗa. Yana cikin irin wannan yawon na sa ne ya iso wani gari da ake kira da Yada Jallonka. Su dai mutanen wannan gari sun kasance su na fama da matsalar wani murgujejen dodo maɓarnaci mai shigowa cikin garin duk daren Allah domin ya yi ɓarna. Duk dare ya na shigowa ya aikata duk abinda ya ga dama akan anfanin gonarsu ,da dabbobin su kai har ma da mai tsauyai ko baƙo daga cikin mutanen. Tun a bayan gari ya ke fara wata waƙa ya na cewa: "Wa yai ya ni, a garin nana? Wa yai ya ni, ni Dodo? Idan ya yi wannan waƙa ya gaji babu wanda ya tanka masa sai kuma ya baiwa kan amsa ta hanyar kuma rera: "Babu ya ni, a garin nana Babu ya ni ai sun san ni" Sai kuma ya bushe da wata irin dariya da miyagun maƙetata. Bayan saukar Auta a wannan gari ...

ƳAR BORA DA KIFANYA

Image
YAR BORA DA KIFANYA Wata yarinya ce ta taso a gidan da aka mayar da mahaifiyarta bora, duk wani aikin wahala na gidan da ita da mahaifiyarta ne su ke yin sa ga tsamgwama.ga kuma makirci. Yayinda ita kuma Mowaa da ƴaƴanta suna kwance ma ake kai musu abinci bayan an gama. Ana cikin wannan hali, wata rana sai mai gidan ya sayo kifaye daga wajen masu su mai tarin yawa. Ya na kawowa ya ajiye sai Mowa ta ce da ƴar bora cikin isa da mallaƙa "Ɗauki kifayen nan ki je rafi ki wanko mana su tatas kuma na riga na ƙirga su, idan na ga babu guda ɗaya sai na lahira ya fi ki jin daɗi" Kasancewar lokacin ɗari ne, Jikin yarinya na karkarwar saboda ɗari da kuma ta tsoron faɗan maƙetaciyar kishiyar mahaifiyarya, ta ɗebi kifi ta tafi rafi. Ta na cikin wanke kifi ne kawai sai ta ga guda ɗaya ta tashi da rai har ta na yi mata magana ta na cewa " Ƴarinya ki dubi Allah ki bar ni na je na shayar da ariraina a cikin ruwa amma na yi miki alƙaearin zan komo" Yarinyar ta saki kifanya a ckin ruwa...

KASSU ATTAJIRI

Image
KASSU ATTAJIRI A can garin Ƙauran Namanzo anyi wani babban attajiri mai suna Kassu, wanda ya mallaki dukiyar da ko shi kan sa ma bai san yawanta ba. Ana kiransa da Kassu ne saboda an haife shi ranar da kasuwa ke ci a garinsu. Wasu jama'a na zargin cewa wannnan dukiyar ta sa wai ta samo asali ne daga aljanu. Wai ana cewa wata aljana ya taɓa taikawa shi ne ita ma ta ci alwashin cewa sai ta saka masa kuma ta dinga taimaka masa wajen samun buɗi ta ko ina. Wasu kuwa su ka ce wai wani malaminsa ya taɓa yi wa wata bajinta shi ne shi kuma malamin ya roƙa masa arziƙi da shuhura a duniya. To koma dai wannene daga ciki haƙiƙa Kasuu ya gawurta ta yanda har yau har kwanan gobe an rasa wanda zai iya kawowa ko kusa da inda ƴaƴan jikokinsa su ke tashen kuɗi a halin yanzu a faɗin ƙasar ma baki ɗaya. A lokacin da yake raye, Kassu ya taimakwa talaƙwa da dama su ma har sai da su ka zama manyan attajirai. Idan ya fitar da zakkarsa ra sgekara ya kan nemi talaka tiƙos amma wanda ya ne fafutuka a wata har...